Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto Bahram Qasimi yana fadar haka a jiya Lahadi, ya kuma kara da cewa yaki da yan ta'adda wanda gwamnatin kasar Iran da sauran kawayen kasar Siriya suka yi a kasashen Iraqi da Siriya ne ya dawo da zaman lafiya a wadannan kasashe, amma yaki don ganin bayan wadan nan kungiyoyi kwatakwata yana bukatar hadin kai daga kasashen duniya gaba daya.
Qasimi ya kara da cewa, zaman lafiya da aka sami a birnin Paris na kasar Farana da wasu manya-manyan biranen kasashen Turai ya samu ne don kokarin yakar kungiyoyin yan ta'adda wanda kasar Iran da sauran kawayen gwmnatin kasar Siriya suka yi a nan yankin gabas ta tsakiya.
Daga karshe Qasimi ya kammala da cewa dole ne kasashen Turai su fahinci cewa halayensu ne ya samanda kungiyoyin yan ta'adda a duniya, tunda har yanzun da muke magana kasashen turai suna bawa wasu kungiyoyin yan ta'addar mafaka.